Hukumar Tsaro ta Farin Kaya, SSS, ta kama wani mai amfani da kafar facebook, Ibrahim Sarki Abdullahi sakamakon tsokanar ƴar gwagwarmayar nan mai rajin kare haƙƙin mata, Zainab Nasir a kan ra’ayinta kan aure.
Wata majiya daga hukumar ta baiyanawa jaridar DAILY NIGERIAN cewa Abdullahi na nan ya na shan tuhuma a kan yadda ya ke tsokanar mutane a kafar sadarwa.
Tun a baya ne dai Zainab ta taɓa baiyana matsayinta a kan aure, in da ta ce “aure ba nasara ba ne”, batun da ya haifar da cecekuce a kafafen sadarwa.
Haka-zalika a ranar da Malala Yousafzai ta baiyana yin aurenta, jama’a da yawa sun tuna Zainab a kan matsayinta kan aure.
Idan za a tuna, a kwanannan ne dai Abdullahi ya wallafa hoton Zainab ɗin a facebook tare da wani saƙo da ya ke cewa “Malala ta shushe mu”, lamarin da ya kufular da ƴar rajin kare haƙƙin mata ɗin har ta yi barazanar maka shi a kotu.
Amma daga bayan, bayan Zainab ta yi barazanar maka shi a kotu, sai Abdullahi ya yi wuf ya goge saƙon, amma ina, haƙar shi ba ta cimma ruwa ba, don tuni jami’an farin kaya su ka cafke shi.